An faɗaɗa rundunonin sama da na ƙasa yayin ƙaruwa hare-haren al-Shabaab

Turkiyya ta ƙara tura sojoji Somaliya domin yaƙi da ta’addanci

Jami’an tsaron Turkiyya sun ce ƙasar ta ƙarfafa tsarin tura sojojinta zuwa Somaliya ta hanyar faɗaɗa rundunonin sama da na ƙasa da ke tallafa wa ƙasar a yaƙin da take yi da ta’addanci, musamman yayin da hare-hare ke ƙaruwa a Mogadishu da kewaye da birnin. TRT Hausa

A cewar jami’an, Rundunar Haɗin Gwiwar Somaliya da Turkiyya tare da Sashen Rundunar Sojin Sama na Turkiyya na ci gaba da tallafa wa Somaliya ta fuskar horo, shawarwari da kayan aiki domin ƙarfafa ƙarfin yaƙi da ‘yan ta’adda. TRT Hausa

Sun ƙara da cewa an tura ƙarin sojoji da kayan aiki domin ƙarfafa rundunar sojin saman Turkiyya da ke Somaliya, matakin da zai taimaka wajen ci gaba da daƙile ayyukan ta’addanci a ƙasar. TRT Hausa

Somaliya dai na fama da ƙungiyar al-Shabaab sama da shekaru goma, duk da ayyukan soji da dakarun ƙasa tare da na Tarayyar Afirka da ƙawayen ƙasashen waje ke yi, inda kungiyar ke ci gaba da kai hare-haren bama-bamai da kisan kai. TRT Hausa

Turkiyya ta kasance ɗaya daga cikin manyan abokan Somaliya, inda take da babban sansanin horar da soji a Mogadishu tare da horas da dubban sojojin Somaliya da ba su kayan aiki da tallafin fasaha. TRT Hausa

Jami’an Turkiyya sun bayyana cewa manufar ƙarin tura sojojin ita ce taimaka wa Somaliya gina ingantaccen tsarin tsaro mai ɗorewa domin tabbatar da zaman lafiya na dogon lokaci da hana al-Shabaab sake ƙarfafa kanta. TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#