Dollar

41,2861

0.06 %

Euro

48,4058

0.05 %

Gram Gold

4.768,6700

0.27 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Kamfanin dillancin labaran ƙasar, ANP ya rawaito cewa Shugaban Ƙasar ya naɗa ɗan jarida, Ibrahim Gambo Diallo a matsayin shugaban hukumar ta ONC.

Tiani ya kafa sabuwar hukumar sa ido kan kafafen yaɗa labarai ta Nijar

Shugaban ƙasar Nijar, Janar Abdourahamane Tiani ya rattaɓa hannu kan dokar da ta kafa hukumar sa ido kan kafafem yaɗa labarai ta ƙasar (ONC).

Hukumar ta ONC za ta yi aiki ne domin kare ‘yancin ‘yan jarida da kuma kafafen yaɗa labarai tare da bai wa kowa ikon amfani da kafafen yaɗa labarai da kuma tabbatar da cewa kafafen na biyayya ga ɗa’ar aikin jarida a ƙasar Nijar, In ji kamfanin dillancin labaran ƙasar, ANP.

Jim kadan bayan sanar da kafa sabuwar hukumar e kuma, sai Shugaba Tiani ya naɗa wani ƙwararren ɗan jarida Ibrahim Manzo Diallo a matsayin shugaban hukumar ta ONC.

Kazalika hukumar na da alhaƙin kare a’adu musamman tallata yarukan ƙasa a kafafen yada labarai domin tabbatar da cewa ana mutunta ɗabi’u da al’adu masu kyau a kafafen yaɗa labaran.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#