Dollar

41,2794

0.05 %

Euro

48,3397

-0.06 %

Gram Gold

4.811,3500

0.01 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Harin ya faru da safe a Ramot Junction kan titin Yigal, inda aka raunata kimanin mutum 15, kamar yadda wata sanarwa ta baya daga MDA ta bayyana.

Mutum biyar sun mutu a hare-haren da aka kai Birnin Ƙudus

Wasu 'yan bindiga sun buɗe wuta a tashar mota a Gabashin Birnin Ƙudus da Isra'ila ta mamaye a ranar Litinin, inda suka kashe mutum biyar tare da raunata wasu da dama.

Rundunar 'yan sandan Isra'ila ta bayyana cewa an kashe 'yan bindigar biyu a wurin da lamarin ya faru.

Hukumomi sun ce mutum bakwai suna cikin mawuyacin hali.

Cikin waɗanda suka mutu akwai wani mutum mai kimanin shekara 50 da kuma wasu maza uku masu shekaru kusan 30, kamar yadda wata sanarwa daga hukumar agaji ta MDA ta bayyana, tana mai cewa tana ba da kulawar lafiya ga wasu daga cikin wadanda suka ji rauni.

Harin ya faru da safe a Ramot Junction kan titin Yigal, inda aka raunata kimanin mutum 15, kamar yadda wata sanarwa ta baya daga MDA ta bayyana.

Firaminista Benjamin Netanyahu yana gudanar da taro don tantance halin da ake ciki bayan harin, kamar yadda ofishinsa ya bayyana.

"Muna tabbatar da cewa wannan aiki martani ne na halas ga laifukan Isra'ila na mamaye ƙasa da kisan kiyashi da take yi wa mutanenmu," in ji kungiyar 'yan gwagwarmaya ta Falasdinawa, Hamas a wata sanarwa.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#