Sport
Dollar
41,2684
0.01 %Euro
48,6593
0.01 %Gram Gold
4.810,7500
0 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Qatar ta yi Allah-wadai da abin da ta kira harin matsorata da Isra'ila ta kai kan kasarta.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayar da rahoton cewa, Isra'ila ta tabbatar da cewa ta kai wani hari kan manyan shugabannin kungiyar Hamas, ko da yake ba ta bayyana inda aka kai harin ba.
Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da kafafen yada labarai daga Qatar suka ce an ji ƙarar fashewar wasu abubuwa a Doha babban birnin kasar, tare da turnuƙin hayaƙi da ke tashi sama.
Wani babban jami'in gwamnatin kasar Isra'ila ya shaida wa kafofin yada labaran kasar cewa harin ya rutsa da mataimakin shugaban kungiyar Hamas Khalil al-Hayya da kuma babban jami'in kasar Zaher Jabareen.
Wata tawagar shugabannin Hamas ta tsallake rijiya da baya a harin na Doha, kamar yadda wani babban shugaban kungiyar ya shaida wa Al Jazeera.
Jami’an Isra’ila sun kuma shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an kai harin ne kan shugabannin Hamas a Qatar, sai dai ba a sami karin bayani kan asarar rayuka ko kuma girman harin ba.
Comments
No comments Yet
Comment