Rahoto ya ce kusan rabin labaran da aka wallafa a 2025 na ɗauke da son kai

Bincike ya gano nuna son kai kan Musulmai a kafafen watsa labaran Birtaniya

Wani sabon bincike ya nuna cewa kusan rabin rahotannin kafafen watsa labarai na Birtaniya da suka shafi Musulmai a shekarar 2025 na ɗauke da wani mataki na nuna son kai.

Binciken da Cibiyar Sanya Ido Kan Kafafen Watsa Labarai (CfMM) ta gudanar ya gano cewa kusan labarai 20,000 daga cikin jimillar labarai 40,913 da manyan kafafen watsa labarai 30 suka wallafa sun ƙunshi wani nau’in nuna son kai.

Rahoton ya kuma bayyana cewa kusan kashi 70 cikin ɗari na labaran sun haɗa Musulmai ko Musulunci da halaye ko matsaloli marasa kyau.

Binciken ya nuna cewa wasu kafafen watsa labarai masu ra’ayin rikau ne suka fi nuna irin wannan son kai a labaransu.

Daga cikin kafafen da rahoton ya ambata akwai The Spectator, GB News, The Telegraph, Jewish Chronicle, Daily Express, The Sun, Daily Mail da The Times.

Darektan CfMM, Rizwana Hamid, ta ce rahoton ya gabatar da hujjoji masu tayar da hankali game da yadda ake nuna Musulmai a cikin jaridun Birtaniya.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#