Iran Ta Ce Ba Za Ta Firgita Da Barazanar Soja Ba

Khamenei Ya Gargadi Amurka Kan Yiwuwa Yaƙin Yanki

Jagoran addini na Iran, Ali Khamenei, ya yi gargaɗin cewa duk wani farmakin soja da Amurka za ta kai kan Iran zai iya haifar da yaƙi da zai bazu a duk faɗin yankin Gabas ta Tsakiya, inda ya bayyana hakan a wata ganawa da aka yi a Tehran a ranar Lahadi. TRT Hausa

Khamenei ya yi wannan jawabi ne a gabanin bikin cikar shekaru 47 na Juyin Juya Halin Musulunci na 1979, yana mai cewa tura jiragen ruwan yaki na Amurka zuwa Tekun Fasha ba sabon abu ba ne kuma ba zai razana Iran ba. TRT Hausa

Ya ce jami’an Amurka sun sha yin barazana a baya ta hanyar cewa “duk zaɓi na kan tebur”, ciki har da amfani da ƙarfin soja, yana mai nuni kai tsaye ga Shugaban Amurka Donald Trump. TRT Hausa

Khamenei ya jaddada cewa Iran ba ta firgita da irin waɗannan barazana, yana mai cewa al’ummar Iran ba sa jin tasirin kalaman tsoratarwa daga ƙasashen waje. TRT Hausa

A gefe guda, Shugaba Donald Trump ya rubuta a kafar sada zumunta cewa wani ƙaton jirgin ruwa mai ɗaukar jiragen sama na Amurka na kan hanyarsa zuwa yankin, tare da kira ga Iran da ta shiga tattaunawa nan take. TRT Hausa

Wannan bayani ya ƙara haifar da hasashen yiwuwar farmakin soja, tare da jawo martani mai ƙarfi daga jami’an Iran da kuma hanzarta harkokin diflomasiyya a yankin. TRT Hausa

Khamenei ya ce Iran ba za ta fara yaƙi ba kuma ba ta da niyyar kai hari kan kowace ƙasa, amma zai mayar da martani mai ƙarfi ga duk wanda ya kai mata hari ko ya cutar da ita. TRT Hausa

Dangane da zanga-zangar adawa da gwamnati da aka samu kwanan nan, Khamenei ya bayyana su a matsayin kamar “juyin mulki” da aka dakile, yana mai zargin Amurka da Isra’ila da tallafa wa abin da ya kira masu tayar da tarzoma. TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#