Publication : 27 January 2026
Update : 27 January 2026
An ceto su a yankin iyakar Zango yayin ƙoƙarin safararsu zuwa Libya da Turai
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) a Daura ta ceto mutum 22 daga hannun masu safarar mutane a yankin iyakar Zango na Jihar Katsina, bayan samun bayanan sirri daga al’ummomin kan iyaka kan zirga-zirgar da ake yi ba bisa ƙa’ida ba. (TRT Hausa)
Kwamandan rundunar NIS a kan iyakar Jibia, Haruna Zakirai, ya ce jami’an hukumar tare da ‘yan sandan Daura sun kai ɗauki cikin gaggawa, inda suka ceto mutanen a wani gini da ba a kammala ba a ƙauyen Maibara da ke ƙaramar hukumar Zango. (TRT Hausa)
A cewarsa, waɗanda aka ceto sun haɗa da mata 11 da maza 11 masu shekaru tsakanin 17 zuwa 35, daga jihohi daban-daban na Nijeriya ciki har da Legas, Osun, Rivers, Kwara, Katsina, Imo, Ondo, Benue da Babban Birnin Tarayya Abuja. (TRT Hausa)
Binciken farko ya nuna cewa ana shirin safarar mutanen ta hanyoyi marasa tsari zuwa Libya, daga nan kuma zuwa Turai, inda aka yaudare su da alkawarin samun damar tattalin arziki mai kyau. (TRT Hausa)
Zakirai ya ce wani ɗan ƙasar Togo na cikin waɗanda aka ceto kuma za a mayar da shi ƙasarsa bayan kammala bincike, yayin da babban jagoran masu safarar da aka fi sani da “Cargo” ya tsere kuma ana nemansa ruwa-a-jallo. (TRT Hausa)
Hukumar Shige da Fice ta sake jaddada ƙudirinta na yaƙi da safarar mutane da shige da fice ba bisa ƙa’ida ba, tare da kira ga jama’a da su bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai kan masu aikata irin waɗannan laifuka. (TRT Hausa)
Drone hits gas storage tanker at Egypt's Mediterranean port
A drone has hit a US-owned gas storage tanker at Egypt's Mediterranean port of Damietta, maritime security firm Ambrey said on Wednesday.
List: 25 African cities where US visa applicants must apply elsewhere from August 1, 2026
In mid-July 2026, the US Department of State announced that it would discontinue visa-processing in 25 cities across Africa, with such services assigned to what Washington calls "regional hubs."
DRC audit finds pollution linked to French-British oil firm's operations, ministry says
A government audit into the operations of French-British oil company Perenco in DRC found it responsible for polluting the environment, preliminary findings by the government show.
Most Read
All rights reserved. Newstimetr © 2023