Dollar

41,2781

0.06 %

Euro

48,5788

0.03 %

Gram Gold

4.839,4800

0.34 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Shugaban ƙungiyar NUPENG, Williams Akporeha, ya bayyana ranar Lahadi cewa ƙungiyar za ta ci gaba da  yajin aikin zuwa ƙarshen tattaunawar ƙungiyar da gwamnati ranar Litinin.

Dalilan NUPENG na yin yajin aiki a kan Matatar Dangote

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ma’aikatan da ke dakon man fetur da Gas a Nijeriya (NUPENG) ta ce lallai sai ta shiga yajin aikin sai-baba-ta-gani daga ranar Litinin duk da sa bakin gwamnatin tarayyar ƙasar wajen ba su haƙuri su janye yajin aikin.

Shugaban ƙungiyar NUPENG, Williams Akporeha, ya bayyana a ranar Lahadi cewa ƙungiyar za ta ci gaba da yajin aikin zuwa ƙarshen tattaunawar ƙungiyar da gwamnati a ranar Litinin.

A ranar Jumma’a ne dai ƙungiyar ta bayyana cewa za ta fara yajin aikin ranar 8 ga watan Satumba, lamarin da zai iya janyo rashin mai a ƙasar.

Ta ce za ta hana mambobinta dakon mai a faɗin ƙasar daga ranar Litinin idan har lamarin bai sauya ba.

Amma mene ne ya sa ƙungiyar ta tsunduma cikin yajin aiki?

Ta ɗauki matakin ne sakamakon shirin Matatar Man Dangote na shigo da tankokin dakon mai masu amfani da iskar gas na CNG guda 4,000 domin kai mai ga masu sayarwa da kanta.

Kafin matatar ta ɗauki wannan matakin ta fuskanci ƙalubale na sayar da manta a Nijeriya inda wasu ‘yan kasuwa suke shigowa da tataccen mai daga ƙetare maimakon saya daga matatar.

Bayan haka ne Matatar Dangote ta tsara wani shirin sayar da mai kai-tsaye ga gidajen mai da kuma yi musu dakon mai a kyauta.

A da Matatar Dangote ta ce shirin zai fara aiki ranar 15 ga watan Agusta, sai dai kuma yanzu ta ce shirin zai fara aiki ne da zarar da yawa daga cikin tankokin dakon sun iso Nijeriya.

Ɗaya daga cikin dalilan da ƙungiyar NUPENG ta bayar na shiga yajin aikin shi ne zargin da suka yi wa Matatar Man Dangote na ɗaukar matakan da ke ƙin jinin ‘yan ƙwadago da kuma yin barazana ga hanyar samun direbobin tankokin dakon mai.

Ƙungiyar ta nuna damuwa kan dagewar da Matatar Mai ta Aliko Dangote ke yi cewa sabbin direbobin tankokin da zai shigo da su ba za su samu damar shiga ƙungiyar ƙwadago ba.

Ƙungiyar ta bayyana wannan matakin a matsayin farmaki kan ‘yancin tarayya wanda kundin tsarin mulkin shekarar 1999 ya tabbatar, da kuma keta dokokin ƙwadago na duniya waɗanda Nijeriya ta amince da su.

“Ba za mu iya tsayawa mu zura ido ba yayin da ake lalata ayyukan mambobinmu,” in ji ƙungiyar.

NUPENG ta ce ta tattauna da ƙungiyar masu motocin haya ta Nijeriya da zummar sauya wa Dangote ra’ayinsa, amma dukkan kiraye-kirayenta ba su yi tasiri ba.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#