Dollar

41,2910

0.2 %

Euro

48,4340

0.61 %

Gram Gold

4.758,6800

1.43 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta yi iƙirarin cewa magoya bayan Shugaba Tinubu waɗanda saƙon da Sowore ya wallafa ya ɓata wa rai sun fara zanga-zanga a kan titunan Nijeriya.

Hukumar DSS ta buƙaci shafin X ya cire saƙon da Sowore ya wallafa yana ƙaryata Shugaba Tinubu

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Nijeriya (DSS) ta rubuta wasiƙa ga kamfanin X Corp, mai shafin sada zumunta na X (wanda ake ce wa Twitter a da), tana mai neman kamfanin ya goge wani saƙo da mai fafatuka Omoyele Sowore ya wallafa inda ya ƙaryata Shugaba Bola Tinubu .

A wata wasiƙar da DSS ta wallafa shafinta na X ranar Asabar, hukumar ta zargi Mista Sowore da yin amfani da saƙonsa na X  wajen cin fuskar shugaban ƙasa Tinubu da yi masa rashin mutunci da ba’a.

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X ranar 25 ga watan Agusta, Mista Sowore ya soki ziyarar da shugaban Nijeriya ya kai Brazil da kuma kalaman da shugaban ya yi yayin ziyarar.

“Mai laifi @officialABAT (Bola Tinubu) ya je Brazil inda ya ce babu cin hanci da rashawa a Nijeriya a gwamnatinsa. Ji wani ƙarfin hali na ƙarya ba tare da kunya ba!”— in ji Omoyele Sowore (@YeleSowore) ranar 26 ga watan Agustan shekarar 2025.

Sai dai a wasiƙar da DSS ta aike wa kamfanin X ta ce waɗannan kalaman sun ɓata wa magoya bayan Shugaba Tinubu rai lamarin da ya sa suka yi zanga-zangar rashin amincewa da kalaman na Sowore a kan titunan ƙasar.

Saboda haka, hukumar ta bai wa shafin X wa’adin sa’o’i 24 domin ya cire kalaman Sowore  ko kuma ta ɗauki matakai masu tsauri a kan shafin.

Kalaman Tinubu a Brazil

A lokacin da ya kai ziyara ƙasar Brazil dai, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta yi a Nijeriya sun kawo ƙarshen cin hanci a ƙasar.

“Sauyen-sauyen da na ƙaddamar tun da na karɓi ragamar mulki a Nijeriya suna tasiri sosai. Zan iya bugun ƙirji kan haka. Daga farko sun ba da wahala. Amma a yau sakamakonsu yana haɓaka,” in ji Shugaba Tinubu.

 “Yana daɗa bayyana ga mutane. Mun ƙara yawan kuɗi cikin tattalin arzikinmu. Yanzu babu cin hanci da rashawa. Gwamnan babban bankin [Nijeriya] ya zo nan. Ba sai ka san shi ba kafin ka samu takardun kudin ƙasashen waje da kake buƙata,” in ji shi.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#