Gwamnan yankin ya kai ziyara sansanin sojoji bayan artabun da aka yi da maharan

An daƙile harin ’yan bindiga a filin jirgin Tahoua a Nijar

Gwamnan Yankin Tahoua a Jamhuriyar Nijar, Souleymane Amadou Moussa, ya kai ziyara Sansanin Sojin Sama na 401 da ke filin jirgin saman Tahoua bayan wani hari da ’yan bindiga suka kai da daddare wanda dakarun tsaro suka samu nasarar daƙilewa.

Harin ya faru da misalin karfe 3:05 na asuba lokacin da wasu ’yan bindiga da suka zo kan babura suka yi yunkurin kai farmaki kan filin jirgin. Rahotanni sun ce maharan sun lalata wasu garejin ajiye jirage marasa matuƙa kafin jami’an tsaro su fatattake su.

Hukumomi sun ce a yayin artabun wasu daga cikin maharan sun mutu, yayin da aka kama mutane biyar da ake zargi da hannu a harin, tare da taimakon mazauna yankin. An kuma kwato kuɗi da wasu kayayyaki daga hannunsu.

Gwamnan ya ziyarci wuraren da harin ya shafa tare da duba ɓarnar da aka yi, sannan ya yaba wa jami’an tsaro kan saurin mayar da martani da suka yi wanda ya tilasta wa maharan janyewa.

Ya tabbatar wa jama’a cewa an shawo kan lamarin, kuma rayuwa a yankin Tahoua na ci gaba kamar yadda aka saba, tare da cewa filin jirgin saman na ci gaba da aiki cikin tsaro.

Gwamnan ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su ci gaba da ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar sanar da duk wani abu da ake zargi domin tabbatar da tsaron yankin.

Hukumomi sun ce an kaddamar da bincike kan harin yayin da matakan tsaro ke ci gaba da ƙaruwa a yankin.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 
 
 

.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#