Dollar

40,7086

0.17 %

Euro

47,4348

-0.19 %

Gram Gold

4.444,4400

0.22 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Wata kotu ta musamman a babban birnin Chadi, N'djamena, ta same shi da laifin furta kalaman ƙiyayya da nuna ƙiyayya ga baƙi da kuma tunzura jama’a domin aikata kisan-kiyashi.

An yanke wa tsohon Firaministan Chadi Succes Masra hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari

Wata kotu a Chadi ta yanke wa shugaban ‘yan adawa kuma tsohon Firaminista Succes Masra hukuncin ɗaurin shekaru 20 a gidan yari bayan ta same shi da laifin tayar da rikicin ƙabilanci wanda ya yi sanadin mutuwar fiye da mutum 40 a kudu maso yammacin ƙasar a watan Mayu.

Wata kotu ta musamman a babban birnin Chadi, N'djamena, ta same shi da laifin furta kalaman ƙiyayya da nuna ƙiyayya ga baƙi da kuma tunzura jama’a domin aikata kisan-kiyashi, in ji Francis Kadjilembaye, ɗaya daga cikin lauyoyin kare shi, yayin da yake magana da manema labarai ranar Asabar.

Kotun ta kuma umarci Masra da ya biya tara ta CFA biliyan 1, kimanin dala miliyan 1.8

Masra ya musanta zarge-zarge yayin shari'ar

Lauyoyinsa sun yi iƙirarin cewa masu gabatar da kara sun kasa gabatar da hujjojin da suka tabbatar da hannunsa a cikin lamarin.

A makon da ya gabata, masu gabatar da kara sun nemi kotu ta yanke masa hukuncin shekaru 25 a gidan yari.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#