Sport
Dollar
40,6900
0.17 %Euro
47,4124
-0.2 %Gram Gold
4.439,9800
0.12 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Ranar Laraba ne wani jirgin helikwafta na sojin Ghana ya yi hatsari, lamarin ya yi sanadin rasuwar ministoci biyu da wasu jami'an ƙasar.
Shugaban ƙasar Ghana John Mahama ya dakatar da harkokinsa tare da ayyana makoki na kwanaki uku a faɗin ƙasar sakamakon hatsarin jirgin helikwafta na soji wanda ya kashe manyan jami’an gwamnatinsa a ranar Laraba.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar Ghana ya ambato wata sanarwa daga ministan watsa labarai kuma mai magana da yawun gwamnati, Mista Felix Kwakye Ofosu, tana cewa shugaban ya ɗauki matakin nan-take domin martaba waɗanda hatsarin ya rutsa da su.
Sanarwar ta bayyana cewa ƙasar za ta yi juyayin kwanaki uku daga ranar Alhamis, 7 ga watan Agustan shekarar 2025.
Mista Julius Debra, shugaban ma’aikata a fadar shugaban ƙasar, ya ba da umarnin cewa a yi ƙasa-ƙasa da tutocin ƙasar.
Hatsarin na jirgi mai saukar ungulu na sojin ƙasar Ghana ya faru ne da safiyar Laraba a Adansi-Akrofuom a lardin Ashanti na ƙasar.
Waɗanda suka rasu a hatsarin sun haɗa da Dakta Edward Kofi Omane Boamah, Ministan Tsaro, da Dakta Ibrahim Murtala Mohammed, Ministan Muhalli da Kimiyya da Fasaha, da Alhaji Muniru Mohammed, muƙaddashin mataimakin shugaban gudanarwar harkar tsaro, da Dakta Samuel Sarpong, mataimakin shugaban Jam’iyyar NDC, da kuma Mista Samuel Aboagye, tsohon ɗan takarar majalisar dokoki.
Comments
No comments Yet
Comment