Sport
Dollar
38,8949
0.36 %Euro
43,4533
-0.25 %Gram Gold
3.997,1000
-0.9 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Mutumin ya tayar da bam ɗin ne a daidai lokacin da wasu matasa masu neman shiga aikin soja suka yi jerin-gwano a wajen wani sansanin soji a Mogadishu.
Akalla mutum 11 sun rasa rayukansu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wani ɗan ƙunar-baƙin-wake ya tayar da bam a wajen wani sansanin soja a babban birnin Somaliya, Mogadishu, a ranar Lahadi, in ji wani jami'i.
Harin ya faru ne a sansanin sojojin Somaliya na Damaanyo da ke unguwar Hodan, inda aka kai wa matasa masu neman shiga aikin soja hari yayin da suke jerin-gwano a wajen ginin.
Wani jami'in tsaro daga unguwar Warta Nabada da ke kusa da wurin wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa fararen hula biyu da wasu masu neman shiga aikin soja na daga cikin waɗanda suka mutu a harin. Ya ce an kai waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci.
Kungiyar ta'addanci mai alaka da Al-Qaeda, al-Shabaab, ta ɗauki alhakin kai harin.
Al-Shabaab ta shafe fiye da shekara 16 tana yakar gwamnatin Somaliya, kuma sau da yawa tana kai hare-hare kan jami'an gwamnati da sojoji.
Comments
No comments Yet
Comment