Sport
Dollar
40,9400
0.02 %Euro
47,6570
-0.14 %Gram Gold
4.397,8300
-0.21 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Rahotanni daga Chadi na cewa an cafke wani ƙaramin ɗan cikin wanda ya kafa ƙungiyar Boko Haram, wanda ke jagorantar wani gungun 'yan ta'adda.
An kama wani matashi ɗan Mohammed Yusuf, wanda ya kafa Boko Haram, a ƙasar Chadi, inda ake zargin yana jagorantar wata ƙungiyar ta'addanci, kamar yadda wata majiya ta leƙen asiri da tsohon mamban Boko Haram ta tabbatar.
An kama matashin mai suna Mohammed Yusuf tare da wasu mutane biyar da ake zargin mambobin ƙungiyar ta'addanci ne, wadda aka kafa a Nijeriya, ƙasar da ke makwabtaka da Chadi, shekaru kaɗan kafin haihuwarsa.
Mahaifinsa, Mohammed Yusuf, shi ne wanda ya kafa wannan ƙungiyar ta'addancin.
Boko Haram ta shafe kusan shekaru 15 tana haddasa matsalolin tsoro a yankin Tafkin Chadi, tare da kai hare-hare masu tsanani kan ƙauyuka da sansanonin sojoji a 'yan watannin nan.
Rundunar ‘yan sandan Chadi ta tabbatar da kama mutane shida da ake zargin mambobin Boko Haram ne, amma ba ta tabbatar ko ɗaya daga cikinsu ɗan Mohammed Yusuf ba na.
Matashi ɗan ta’adda
Wata majiya daga fannin leƙen asiri na Nijeriya da ke yankin Tafkin Chadi ta shaida wa AFP a ƙarshen mako cewa sun samu rahoton kama wata ƙungiyar ta'addanci mai mutum shida a Chadi.
"Ƙungiyar tana ƙarƙashin jagorancin Yusuf, ƙaramin ɗan marigayi wanda ya kafa Boko Haram," in ji majiyar.
Comments
No comments Yet
Comment