Sport
Dollar
43,4990
0.19 %Euro
51,6240
-0.9 %Gram Gold
6.788,9600
-9.85 %Quarter Gold
12.225,8700
-6.97 %Silver
116,5000
-28.39 %Abu Khalid, wanda shi ne mataimakin shugaban Boko Haram na biyu a Dajin Sambisa, an kashe shi tare da wasu ’yan ta’adda 10 yayin wani farmaki da aka kai da dare a Jihar Borno.
Sojojin Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa maso Gabas na Operation Hadin Kai sun kashe wani babban jagoran Boko Haram/ISWAP mai suna Abu Khalid.
Abu Khalid, wanda shi ne mataimakin shugaban Boko Haram na biyu a Dajin Sambisa, an kashe shi tare da wasu ’yan ta’adda 10 yayin wani farmaki da aka kai da dare a Jihar Borno.
Jami’in watsa labarai na rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.
A cewarsa: “Bayan ƙasa da awanni 24 da sojoji suka kawar da shahararren kwamandan Boko Haram/ISWAP mai suna Julaibib, wanda ke aiki a yankin Gujba na Timbuktu Triangle, sojojin Sector 1, tare da hadin gwiwar ’yan Civilian Joint Task Force a karkashin Operation Desert Sanity, sun yi arangama da ’yan ta’adda a yankin Komala na Karamar Hukumar Konduga, a yayin wani farmaki da aka kai da dare da misalin karfe 11:00 na dare.
“Abu Khalid mutum ne mai matukar muhimmanci a cikin tsarin jagorancin ’yan ta’adda, inda yake da alhakin tsara hare-hare da kuma kula da kayan aiki a yankin Sambisa,” in ji shi.
A cewarsa, nasarar da sojojin suka samu a wannan farmaki ta kai ga kwato bindigogin AK-47 guda biyar, da ƙundun harsasai, kekuna da dama, da sauran kayayyakin aiki da na abinci, tare da manyan kayayyakin kiwon lafiya.
Uba ya bayyana cewa ba a samu asarar rai a ɓangaren sojoji ba yayin farmakin, inda ya ƙara da cewa ƙwarin gwiwar sojojin na nan daram, yayin da ake ci gaba da ayyukan tsabtace yankuna a Dajin Sambisa, Dutsen Mandara, Timbuktu Triangle, da sauran wuraren ɓuya da aka sani na Boko Haram da ISWAP a yankin Arewa maso Gabas.
Comments
No comments Yet
Comment