An fara diflomasiyyar nukiliya a kaikaice bayan tashin hankali

Iran ta ce tattaunawa da Amurka na nuna ci gaba

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya ce tattaunawar da ƙasar ke yi da Amurka, tare da taimakon ƙasashen yankin, na nuna alamun “ci-gaba,” kamar yadda ya bayyana a ranar Lahadi. TRT Hausa

Pezeshkian ya jaddada cewa tattaunawa ita ce hanyar Iran ta samun mafita ta lumana, yana mai cewa matsayar ƙasar kan batun nukiliya ta ta’allaka ne kan ‘yancin da yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya ta tanada, tare da ƙin amincewa da matsin lamba ko tilastawa. TRT Hausa

Iran da Amurka sun fara wannan tattaunawa ta diflomasiyya a kaikaice a ranar Juma’a, bayan makonni na tashin hankali da barazanar ɗaukar matakin soja daga Shugaban Amurka Donald Trump. TRT Hausa

Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana tattaunawar a matsayin “mafari mai kyau,” yana mai cewa za a ci gaba da ita a Muscat na Oman, tare da jaddada cewa shirin makami mai linzami na Iran ba ya cikin ajandar tattaunawar. TRT Hausa

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#