Dollar

0,0000

%

Euro

0,0000

%

Gram Gold

0,0000

%

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Ƙungiyar ta'addanci ta YPG ta mayar da asibitin Yassin da ke unguwar Sheikh Maqsoud zuwa wani sansani domin ƙarfafa kansu, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Larabawa na Syria ya ambato ma'aikatar lafiya ta ƙasar tana bayar da tabbaci.

Kungiyar ta'addanci ta YPG ta ƙwace iko da wani asibiti a Aleppo, ta kori ma'aikatan lafiya

Kungiyar ta'addanci ta YPG ta kwace asibiti a unguwar Sheikh Maqsoud da ke Aleppo kuma ta kori ma'aikatan lafiya, in ji ma'aikatar lafiya ta Syria.

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Larabawa na Syria (SANA), ma'aikatar lafiyar ta ce a ranar Asabar: “Kungiyar ta'addanci ta PKK da kungiyoyi masu makamai masu nasaba da ita sun kori ma'aikata da likitoci daga Asibitin Yassin a unguwar Sheikh Maqsoud ta birnin Aleppo suka kuma mayar da shi sansanin soja domin ƙarfafa kansu a ciki, bayan sun gudu a kafin Rundunar Sojan Syria ta Larabawa.”

Ma'aikatar ta gargadi fararen-hula da su nisanci wannan wurin, tana jaddada batun tsaro.

A wani bangaren kuma, wata majiyar soja ta shaida wa SANA cewa wani ɗan ta'adda na YPG ya yi ƙunar-baƙin-wake a kusa da rundunar Sojan Larabawa a Sheikh Maqsoud na Aleppo, ba a samu asarar rai a cikin rundunar ba.

Rundunar Sojan Syria a ranar Asabar ta sanar da cewa an kammala sharewa da tabbatara da tsaro a unguwar Sheikh Maqsoud a yayin da ake samun ƙarin tashin hankali da kungiyar ta'addanci ta YPG.

Haɗin kan ƙasa

Tun a ranar Talata, kungiyar ta'addanci ta YPG ta buɗe wuta kan gidajen mutane da ke cikin unguwanni, da wuraren farar-hula da kuma wuraren Sojojin Syria a Aleppo.

Wadannan hare-haren sun kashe aƙalla mutane tara, sun jikkata wasu 55, kuma sun tilasta wa kusan mazauna 165,000 su gudu daga unguwannin Ashrafieh da Sheikh Maqsoud.

A ranar 10 ga Maris ɗin, 2025, fadar shugaban kasar Syria ta sanar da sanya hannu kan yarjejeniya don shigar da kungiyar cikin hukumomin gwamnati, tana sake tabbatar da hadewar ƙasar da kuma kin yarda da duk wani yunkurin rarrabuwa.

Hukumomi sun ce, a watannin da suka biyo baya, kungiyar ba ta nuna wani yunƙurin cika sharudan yarjejeniyar ba.

Gwamnatin ta ƙara kaimi wajen tabbatar da tsaro a fadin ƙasar tun bayan korar gwamnatin Assad a Disambar 2024, bayan shekaru 24 tana kan mulki.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#