Yakin da Isra'ila ke yi a Zirin Gaza - wanda yanzu ya ke kwana na 150 - ya kashe Falasdinawa akalla 30,410, galibi yara da mata, tare da jikkata wasu 71,700.

Kai-tsaye: Mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris ta yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza

0236 GMT — Mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris ta yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza

Mataimakyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris ta yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza tare da bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin wani abu mai muni.

A yayin wani jawabi da aka yi a Alabama na tunawa da shekaru 59 na "Lahadin da aka Zubar da Jini," ranar da jami'an gwamnatin jihar suka kai wa masu zanga-zangar kare hakkin jama'a hari a gadar Edmund Pettus da ke Selma, Harris ta ce tsagaita wutar za ta fitar da masu garkuwa da mutane da kuma ba da damar shigar da taimakon da ake bukata a Gaza.

Ta ƙara da cewa, "Kuma idan aka yi la'akari da ɗumbin wahala a Gaza, dole ne a tsagaita wuta nan da nan na akalla makonni shida masu zuwa, wanda a halin yanzu yake kan teburin tattaunawa."

"Wannan zai ba mu damar gina wani abu mai ɗorewa don tabbatar da cewa Isra'ila ta kasance cikin tsaro da kuma mutunta 'yancin al'ummar Falasdinu na mutunci da 'yanci da cin gashin kai," in ji ta.

0040 GMT Sojojin Isra'ila sun kashe sama da Falasdinawa 127 a wajen karɓar fulawa a Gaza

A baya-bayan nan ne sojojin Isra'ila suka kashe Falasdinawa sama da 127 tare da jikkata sama da 760 a cikin kwanaki biyu kacal ta hanyar kai hari kan fararen hula da ke kokarin karɓar agajin jinƙai, duk da cewa kotun duniya ta ICJ ta umurci Isra'ila da ta inganta yanayin jinƙai a Gaza.

Ko da yake a ranar Alhamis din da ta gabata sojojin Isra'ila sun bude wuta kan taron Falasdinawa da ke jiran manyan motocin dakon kaya a unguwar Al Nabulsi da ke kudancin Gaza.

Kotun ta ICJ ta yanke hukunci kan takaddamar da ke tsakanin jihohi kuma umarninta na da nasaba da doka, amma ba ta da hanyar tabbatar da aiwatar da hukunce-hukuncenta.

Sojojin Isra'ila sun yi iƙirarin cewa mutanen ne suka tunkari sojojinsu, lamarin da suke ganin zai jefa su cikin haɗari, don haka suka mayar da martani ta hanyar buɗe wuta.

#