Tsawon kwanaki 110, Isra'ila tana ci gaba da kai munanan hare-hare a Gaza a yayin da Firaiminista Netanyahu ya lashi takobin ci gaba kai wadannan hare-hare wadanda suka jawo asarar rayuka 25,490 da raunata mutum 63,354.

KAI-TSAYE: Isra'ila ta kashe gomman mutane a sabbin hare-hare da ta kai Gaza — Falasdinu

0200 GMT — Isra'ila ta kashe gomman mutane a sabbin hare-harenta a Gaza — Falasdinu

Kamfanin dillancin labaran Falasdinu na WAFA ya rawaito cewa, hare-haren da jiragen yakin Isra'ila suka kai sun yi sanadiyyar mutuwar fararen-hula da dama tare da raunata wasu a yankuna daban-daban na Zirin Gaza, musamman Khan Younis da ke kudancin kasar.

Akalla fararen-hula bakwai ne akasari mata suka mutu, yayin da wasu kuma suka jikkata bayan da jiragen yakin Isra'ila suka kai hari kan wani gida a yankin Jabalia da ke arewacin Gaza, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na gwamnati ya bayyana.

Hakazalika hare-haren da jiragen Isra'ila suka kai kan wani gida na iyalan Zaml, ya yi sanadin kashe mutane bakwai da suka hada da mata biyar, in ji rahoton kamfanin WAFA.

Kamfanin dillancin labaran ya ce, harin da Isra'ila ta kai ya kashe fararen hula uku tare da jikkata wasu a wani gida da ke yammacin sansanin 'yan gudun hijira na Nuseirat da ke tsakiyar Gaza.

A Khan Younis, Isra'ila ta kashe wani matashi a yankin masana'antu na Gaza da ke yammacin birnin, yayin da jiragen Isra'ila suka yi ruwan bama-bamai kan wata mota a yammacin Rafah, a yankin kudancin kasar, lamarin da ya yi sanadin jikkatar wasu da dama.

Kazalika an kashe fararen hula da dama, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata bayan da jiragen yakin Isra'ila suka kai hari a Gabar Tekun Khan Younis, in ji kamfanin dillancin labarai.

2213 GMT — Yakin Isra'ila a Gaza ba zai haifar da zaman lafiya ko biyayya ba: Turkiyya

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya caccaki kasashen duniya kan rashin dakatar da yakin Gaza da aka yi wa ƙawanya tare da nuna damuwa game da yadda yakin ke yi wa yankin.

Fidan ya jaddada kauce wa yaduwar yakin zuwa wasu yankunan yankin.

"Kwana 109 a cikin wannan rikici, abin kunya ne yadda har yanzu kasashen duniya suka kasa kawo karshen zubar da jinin da ake yi a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, Gaza ta kasance tamkar budadden gidan yari.

"A yanzu kuma filin yaki ne inda firaministan Isra'ila [Benjamin Netanyahu] yake gudanar da ayyukan soji na kashe fararen hula don tsawaita rayuwarsa ta siyasa,” Fidan ya fada wa taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya, gami da batun makomar Falasdinawa.

Fidan ya ce "Hujjar cewa yakin da ake yi a halin yanzu na samar da tsaro ne ga Isra'ila ba ta zama mai gamsarwa ba, amma duk da haka masu wannan hujja ba su taba yin magana kan tsaron Falasdinawa ba ko kuma 'yancin Falasdinu na kare kai."

Da yake jaddada cewa Isra'ila "tana aikata manyan laifukan yaki," Fidan ya ce dole ne a hukunta wadanda suka aikata laifin domin dawo da imani da dokokin kasa da kasa da kuma bin ka'idoji. Fidan ya jaddada bukatar ruruwar yakin.

"Turkiyya ta yi gargadi game da hadarin da ke tattare da bazuwar yakin a ko da yaushe. Yanzu, a yau, hadarin ya zama gaskiya. Abubuwan da suka faru a baya-bayan nan a cikin Bahar Maliya da Yemen da Lebanon da Iraƙi da Syria da Iran da Pakistan suna da matukar tayar da hankali," in ji shi.

Ministan ya bukaci Isra'ila da magoya bayanta da su nemi hanyar diflomasiyya yayin da har yanzu ana iya cimma ta. Fidan ya ce "Yakin da ake ci gaba da yi a Gaza da ma bayansa ba zai iya haifar da zaman lafiya ko kuma mika wuya ba. Muna da alhakin da ya rataya a wuyanmu a tarihi na dakatar da wannan yaki."

"Makomar Gaza ta rataya a wuyan Falasdinawa ne kawai. Tambayar 'kwana-kwanan nan' da ke bukatar kulawarmu ita ce ta yaya za mu iya kiyaye zaman lafiya mai dorewa bisa tsarin samar da kasashe biyu bisa yarjejeniyoyin 1967," "in ji shi.

#