Ali Larijani ya zargi Netanyahu da jawo Amurka cikin rikici, yayin da Pentagon ta ce sojoji shida kacal suka mutu.

Iran ta yi iƙirarin kashe sojojin Amurka 500 a cikin kwanaki biyar na yaƙi

Iran ta yi iƙirarin kashe sojojin Amurka sama da 500 a sabon yaƙi

Ali Larijani ya zargi Netanyahu da jawo Amurka cikin rikici, yayin da Pentagon ta ce sojoji shida kacal suka mutu.

Babban jami’in tsaron Iran, Ali Larijani, ya yi iƙirarin cewa fiye da sojojin Amurka 500 ne aka kashe tun bayan ɓarkewar yaƙin da ya fara ranar Asabar. A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Larijani ya zargi Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da rinjayar Shugaban Amurka Donald Trump domin jefa Amurka cikin wani yaƙi da Iran da ya kira mara adalci.

Larijani ya ce yanzu Trump ya kamata ya yi tunani kan ko Amurka ce yake karewa ko kuma Isra’ila, yana mai cewa an kashe sojojin Amurka sama da 500 cikin kwanaki kaɗan. Sai dai Ma’aikatar Tsaron Amurka Pentagon ta musanta wannan ikirari, inda ta ce sojojin Amurka shida kacal ne suka mutu tun ranar Asabar, huɗu daga cikinsu a Kuwait.

Kalaman nasa na zuwa ne yayin da rikicin tsakanin Iran da Amurka ke ƙara tsananta bayan harin haɗin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar jagoran addinin Iran Ali Khamenei tare da wasu manyan kwamandojin soji. Iran ta ce kusan mutum 1,050 ne suka mutu cikin kwanaki huɗu na yaƙin, ciki har da yara ‘yan makaranta.

Gwamnatin Iran ta sha alwashin ɗaukar fansa mai tsauri kan kisan Khamenei, inda ta fara kai hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan Isra’ila da sansanonin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya. Larijani ya kuma bayyana cewa Iran ta shirya fuskantar yaƙi mai tsawo.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#