Sport
Dollar
41,4171
0.21 %Euro
48,7056
-0.32 %Gram Gold
4.902,8900
1.34 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Kungiyar Hamas wadda ta koka dangane da taurin-kai irin na Netanyahu ta ce makomar mutanen 47 ta danganta ne da irin matakin da shugabannin siyasa na Isra'ila suka ɗauka.
Kungiyar gwagwarmaya ta Falasɗinawa, Hamas, a ranar Asabar ta fitar da wani hoto da ke nuna mutum 47 da ta kama daga Isra'ila, tana mai cewa an ɗauki hoton ne a farkon baya-bayan nan da Isra’ila ta ƙaddamar a kan Gaza.
Hoton ya zo tare da rubutu a cikin Larabci da Ibrananci yana cewa: “Saboda taurin-kai na [Firayim Minista Benjamin] Netanyahu da biyayyar [Babban Hafsan Sojoji Eyal] Zamir, wannan hoton bankwana ne a farkon aikin a Gaza.”
Hamas ta wallafa hoton a shafinta na yanar gizo, tana mai jaddada matsayinta cewa makomar wadanda aka kama tana hannun shugabannin siyasar Isra'ila.
Hamas ta sha nanata cewa tana shirye ta kammala wata yarjejeniya mai ƙarfi da Isra'ila don sakin dukkan waɗanda aka kama daga ɓangarorin biyu da kawo ƙarshen yaƙin Gaza, da tabbatar da janye dakarun Isra'ila gaba daya.
Sai dai, Netanyahu ya sha ƙin amincewa da irin waɗannan shawarwari, yana dagewa kan shirye-shiryen da za su ba shi damar jan lokaci da sanya sabbin sharudda a kowane mataki na tattaunawa.
Comments
No comments Yet
Comment