Sport
Dollar
41,2903
-0.01 %Euro
48,7815
0.35 %Gram Gold
4.901,5400
0.34 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AUC) ya yi gargaɗin cewa harin na iya barazana ga yanayi mai raunin da ake ciki a gabas Ta Tsakiya.
Ƙasashen Afirka da Ƙungiyar Tarayyar Afrika sun yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ta kai ranar Talata kan shugabannin Hamas a Qatar, suna masu gargaɗin cewa ta keta ‘yancin kan ƙasar.
Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AUC) ya yi gargaɗin cewa harin zai iya barazana ga yanayi mai rauni da ake ciki a Gabas Ta Tsakiya.
Mahmoud Ali Youssouf ya yi nuni da rawar da Qatar ke takawa a wajen shiga tsakani na diflomasiyya yana mai kira da “a sabunta tattaunawa domin samun zaman lafiya na adalci mai ɗorewa a Gabas Ta Tsakiya”.
Ministan Harkokin Wajen Masar ma ya bayyana harin na Isra’ila a matsayin “tsabar keta dokar ƙasa da ƙasa da kuma ‘yancin kan ƙasa.”
‘Misali mai haɗari’
Comments
No comments Yet
Comment