Publication : 7 March 2026
Update : 7 March 2026
Fargabar tangarɗar samar da mai bayan rikicin Amurka, Isra’ila da Iran ta girgiza kasuwannin duniya
Farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya ya yi tashin gwauron zabo a ranar Juma’a sakamakon fargabar tangarɗar samar da mai da kuma matsalolin sufuri da suka biyo bayan rikicin da ke ƙara tsananta a Gabas ta Tsakiya.
Rikicin da ya ɓarke tsakanin Amurka da Isra’ila a kan Iran tare da martanin ramuwar gayya daga Tehran a yankin Gulf ya janyo tashin hankali a bangarorin makamashi da sufuri na duniya, lamarin da ya haifar da rufe Mashigar Hormuz.
Rahotanni sun nuna cewa farashin ɗanyen mai ya kai dala 92.69 a kowace ganga, inda ya ƙaru da kashi 8.5 cikin 100 a rana guda, kuma kusan kashi 30 cikin 100 cikin mako ɗaya.
Haka kuma farashin ɗanyen man West Texas Intermediate (WTI) ya tashi da sama da kashi 12 cikin 100 zuwa fiye da dala 90 a kowace ganga, wanda ake cewa shi ne mafi girman tashin mako-mako da aka taɓa gani.
Mashigar Hormuz na daga cikin muhimman hanyoyin jigilar mai a duniya, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na ɗanyen mai da iskar gas na duniya ke bi ta wannan hanya. Amma rahotanni sun nuna cewa zirga-zirgar jiragen ruwa ta kusan tsaya cik a yankin sakamakon rikicin.
Da farko wasu ‘yan kasuwa sun yi zaton rikicin zai kasance na ɗan lokaci kaɗan, amma bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa dole ne Iran ta “miƙa wuya” kafin a kawo ƙarshen yaƙin, fargabar tsawaitar rikicin ta ƙaru.
Daraktar bincike a kamfanin XTB, Kathleen Brooks, ta ce kalaman Trump sun rage fatan cewa rikicin zai warware cikin gaggawa, abin da ya sa farashin mai ya ci gaba da tashi a kasuwannin duniya.
Tushen labari: Newstimehub
Uganda still at risk from Ebola spread in DR Congo: WHO
Uganda remains at risk from the spread of Ebola in the neighbouring DRC, the WHO said on Wednesday.
Five people killed as suspected terrorists ambush police patrol in northern Kenya
Suspected terrorists ambushed a patrol in northeastern Kenya, killing five people, including four police officers.
Uganda hosts regional summit to discuss Somalia AU peace mission facing transition
The African Union mission has been making security gains against the Al Shabaab terrorist group in Somalia and its mandate is due to end in December 2026.
Most Read
All rights reserved. Newstimetr © 2023