Mutane da dama sun tsere zuwa Jihar White Nile yayin da rikicin Sudan ke ƙara tsananta
Aƙalla mutum 570 sun tsere daga gidajensu a birnin Kadugli da ke Kudancin Kordofan cikin kwanaki uku sakamakon tsananin rikici, a cewar Hukumar Kula da Masu Ƙaura ta Duniya (IOM).
Sanarwar ta ce mutanen sun bar gidajensu daga ranar 8 zuwa 10 ga Janairu bayan da hare-hare suka ƙara ƙamari a birnin, inda galibinsu suka nufi Jihar White Nile da ke Kudancin Sudan domin samun mafaka.
IOM ta bayyana halin da ake ciki a Kadugli a matsayin mai cike da rashin tabbas da haɗari, tana mai cewa tawagoginta na ci gaba da sanya ido kan abubuwan da ke faruwa a yankin.
Hukumar ta kuma ce adadin mutanen da suka fice daga gidajensu a jihohin Kordofan uku – Arewa, Yamma da Kudu – ya kai 64,890 tsakanin 25 zuwa 30 ga Oktoban 2025 sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta.
Rikicin Sudan da ya ɓarke tun watan Afrilun 2023 tsakanin sojojin ƙasar da mayaƙan Rapid Support Forces (RSF) ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyin mutane da muhallansu.
Tushen labari: Newstimehub