Sport
Dollar
42,1021
0.01 %Euro
48,3839
0.04 %Gram Gold
5.386,2900
1.05 %Quarter Gold
9.055,1100
0.33 %Silver
65,0200
1.88 %Harin na zuwa ne a yayin da mayaƙan RSF ke ƙara zafafa kai hare-hare a garin, inda dakarun gwamnati kuma suke ƙoƙarin mayar musu da martani.
Wani hari da aka kai kan taron jana'iza a birnin El Obeid da ke yankin Kordofan na tsakiyar Sudan ya yi ajalin mutane 40, in ji ofishin agaji na Majalisar Ɗinkin Duniya.
Sanarwar da aka fitar ba ta fayyace ranar da harin ya faru ba ko kuma wanda ke da hannu a kai shi, amma ya zo ne a daidai lokacin da mayaƙan RSF suka bayyana cewa a shirye suke su kai hari birnin, inda sojojin suka taru a wani yunƙuri na korar su.
"Yanayin tsaro a yankin Kordofan na ci gaba da taɓarɓarewa," in ji Ofishin Kula da Harkokin Jinƙai a ranar Laraba.
Jihohi uku na Kordofan - Arewa, Yamma, da Kudu - sun shaida mummunan rikici tsakanin sojojin Sudan da 'yan bindigar RSF.
Mayaƙan na RSF sun kuma kama garin Al Fasher, babban birnin Jihar Arewacin Darfur, a ranar 26 ga Oktoba kuma sun yi wa fararen-hula kisan gilla, a cewar ƙungiyoyin cikin gida da na ƙasashen waje, wanda ya haifar da gargaɗin cewa ƙwace iko da yankin zai iya ƙara raba ƙasar da yaƙi ya ɗaiɗaita.
Tun daga watan Afrilun 2023, sojojin Sudan da RSF suka afka cikin yaƙin basasa wanda ya kashe dubban mutane, ya raba miliyoyin mutane da muhallansu, sannan ya haifar da ɗaya daga cikin mawuyacin halin jinƙai da ya fi muni a duniya.
Comments
No comments Yet
Comment