Sport
Dollar
43,1987
0.04 %Euro
50,4018
0.19 %Gram Gold
6.418,1400
-0.2 %Quarter Gold
10.596,7200
-0.12 %Silver
126,5600
-2.28 %‘Yanta’adda sun kashe mutane 14, rabin su yara ƙanana a wani hari da suka kai a yankin arewa maso yammacin Kamaru inda ake magana da Turancin Ingila a ranar Talata, in ji kafar watsa labarai ta gwamnati.
‘Yanta’adda sun kashe mutane 14, rabin su yara ƙanana a wani hari da suka kai a yankin arewa maso yammacin Kamaru inda ake magana da Turancin Ingila a ranar Talata, in ji kafar watsa labarai ta gwamnati.
An kai mummunan harin ne a ƙauyen Guidado.
“A safiyar nan… harin da ‘yanta’adda suka kai wa fararen-hula ya yi ajalin mutane 14 da suka haɗa da namiji babba guda 1, mata manya shida da yara ƙanana bakwai da ke da shekaru tsakanin biyu zuwa 11,” kamar yadda Tashar CRTV ta ruwaito gwamnan yankin arewa maso yamma Adolphe Lele Lafrique na faɗa.
“An kwashi mutane 14 zuwa asibitocin da ke maƙotaka da ƙauyen don kula da lafiyarsu,” in ji gwamnan, yana mai ƙarawa da cewa Shugaba Paula Biya ya bayar da umarnin da a ɗauki matakin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
'Majalisar Ɗinkin Duniya'
‘Yan a-ware da ke neman ‘yancin kai a yankin Kamaru mai magana da Turancin Ingila na yawan yi garkuwa ko kashe ‘yansiyasa, ma’aikatan gwamnati da malaman makaranta da suke zargi da haɗa baki da gwamnati.
Sai dai gwamnati ta sake nanata cewa Kamaru ƙasa ce dunƙulalliya.
Comments
No comments Yet
Comment