Zanga-zanga ta ɓarke a Kano kan hukuncin da Kotun Daukaka Kara ta yanke kwanan nan kan zaben gwamnan jihar.
Zanga-zanga ta ɓarke a Kano kan hukuncin da Kotun Daukaka Kara ta yanke kwanan nan kan zaben gwamnan jihar.
Rahotanni sun ce 'yan sanda sun yi ƙoƙarin tarwatsa masu zanga-zangar a unguwar Dan Agundi da ke cikin birnin Kanon.
Zanga-zangar na zuwa ne bayan bayyanar kwafi na hukuncin Kotun Daukaka Kara, wanda ake zargin ya saɓa wa hukuncin baki da ta sanar a makon da ya gabata, inda ta jaddada hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe na kwace nasarar Abba Kabir Yusuf na NNPP, ta bai wa Nasiru Gawuna na PDP.
A bidiyoyin da TRT Afrika ta gani a shafukan sada zumunta na zanga-zangar da aka yada, an ga mutane suna gudu a daidai titin Gidan Murtala, sakamakon harba hayaki mai sa hawaye da ƴan sanda ke yi.
A makon da ya wuce ne Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin da Kotun Sauraron Kararrakin Zabe ta fara yi tun farko na soke zaben Abba Kabir Yusuf, a ranar 30 ga waran Satumban 2023.