A shirye Turkiyya take ta zama kasa mai tabbatar da zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Falasdinu, in ji Shugaba Erdogan na Turkiyya.

Ya kamata Netanyahu, 'mai kashe mutanen Gaza,' ya fuskanci shari'a kan aikata laifukan yaki: Erdogan

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce ya kamata Firaministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya fuskanci shari'a kan zamowarsa "mai aikata laifukan yaƙi," in ji shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, yana mai kiransa da "mai kashe mutanen Gaza."

"Ba za mu bari a manta da batun mallakar makamin nukiliyar Isra'ila ba," in ji Erdogan da yake jawabi a wajen bude taron Ƙungiyar Hadin kan Ƙasashen Musulmai ta OIC a Istanbul a ranar Litinin.

Waɗanda ke yin biris da kashe-kashen da ake yi a Gaza ta hanyar ƙin cewa komai, har ma suke halasta hakan a karkashin kungiyar Hamas, ba su da wata magana da za su yi da sunan nuna tausayin bil'adama, in ji Erdogani a taron ministoci na 39 na Kwamitin Tattalin Arziki da Kasuwanci na OIC.

"Isra'ila ba ga kisan kai kawai ta tsaya ba, har ma sata tana yi," a cewar Erdogan, yana mai ƙarawa da "Ba za mu sake barin Isra'ila ta sake mamayar Gaza ba."

"Akwai wani tsari na duniya da ke kare muradun ƙasashe ƙalilan. Akwai buƙatar sauya tsatrin MDD da ke baibaye da maguɗi."

Shugaban na Turkiyya ya ce ƙin jinin Musulunci yana watsuwa kamar wata annoba a Ƙasashen Yamma.

A shirye Turkiyya take ta zama ƙasar da za ta shiga tsakani don samar da tattaunawar zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Falasɗinu, ya ƙara da cewa.

"Gaza yankin Falasɗinu ne, Gaza mallakin Falasɗinawa ce kuma za ta ci gaba d akasancewa haka har abadam" in ji shugaban ƙasar Turkiyyan.

"Waɗanda suka kutsa Gaza za su nemi kutsawa wasu wuraren a gobe. Mai kisan mutanen Gaza Netanyahu ya bayyana cewa yana da muradun faɗaɗa mamayarsa," Erdogan ya faɗa.

#