Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yi maraba da sulhun da aka yi tsakanin Ethiopia da Somalia wanda Turkiyya ta jagoranta a Ankara ranar Laraba.
Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yi maraba da sulhun da aka yi tsakanin Ethiopia da Somalia wanda Turkiyya ta jagoranta a Ankara ranar Laraba.
Turkiyya ta jagoranci yin sulhu tsakanin ƙasashen biyu da ke maƙwabtaka da juna bayan sun kwashe kusan shekara guda suna tayar da jijiyoyin wuya.
Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, wanda ya karɓi baƙuncin Firaministan Ethiopia Abiy Ahmed da shugaban ƙasar Somalia Hassan Sheikh Mohamud ranar Laraba, ya bayyana sulhun a matsayin wanda ke cike da "tarihi."
Ranar Alhamis, Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, ya bayyana sulhun a matsayin wani mataki "mai matuƙar muhimmanci da nuna dattako."
'A aiwatar da yarjejeniyar ba tare da ɓata lokaci ba'
"Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat ya yi maraba da sanarwar da Shugaban Somaliya Hassan Sheikh Mohamud, da Firaministan Jamhuriyar Demukuradiyyar Habasha Abiy Ahmed Ali suka sanya wa hannu a ranar 11 ga Disamba, 2024 a Ankara, a karkashin jagorancin Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan,"in ji AU a cikin wata sanarwa.
Kungiyar ta AU ta kara da cewa, "Shugaban hukumar na maraba da wannan muhimmin da ke da matukar muhimmanci na shugabannin Somaliya da Habasha."
Kungiyar ta ci gaba da cewa Faki "yana matukar karfafa musu gwiwa wajen aiwatar da matakan da suka dace ba tare da bata lokaci ba."
"Shugaban ya kara da taya Shugaba Tayyip Erdogan murna bisa goyon bayan da ya bai wa bangarorin biyu bisa kudurinsu na warware sabanin da ke tsakaninsu ta hanyar tuntubar juna da tattaunawa, domin cim ma moriyar kasashensu da al'ummominsu."