Ƙasashen Mali da Burkina Faso da ke maƙwabtaka da Nijar - wadanda su me sojojin da suka ƙwace mulki a shekarar 2020 da 2022 ke mulki a ƙasashen, sun yi alkawarin bayar da hadin kai ga jagororin juyin mulkin Nijar.

Shugaban Sojin Nijar ya kai ziyara kasar waje karon farko tun bayan juyin mulki

Shugaban mulkin sojan Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya isa kasar Mali domin ganawa da takwaransa Kanar Assimi Goita, a ziyararsa ta farko da ya kai wata ƙasa tun bayan da ya ƙwace mulki a watan Yuli, kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rawaito a ranar Alhamis.

Ƙasashen Mali da Burkina Faso da ke maƙwabtaka da Nijar - wadanda su me sojojin da suka ƙwace mulki a shekarar 2020 da 2022 ke mulki a ƙasashen, sun yi alkawarin bayar da hadin kai ga jagororin juyin mulkin Nijar.

A cikin watan Satumba ne kasashen yankin Sahel guda uku suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar da ta ƙunshi tanadin kare juna a kan duk wani harin da za a kai kan ɗaya daga cikinsu.

Suna kuma shirin karfafa dangantakar tattalin arziki.

Haka kuma gwamnatocin sun haɗa kai wajen yaƙi da ta'addanci a ƙasashensu.

#