Ƙasashen Mali da Burkina Faso da ke maƙwabtaka da Nijar - wadanda su me sojojin da suka ƙwace mulki a shekarar 2020 da 2022 ke mulki a ƙasashen, sun yi alkawarin bayar da hadin kai ga jagororin juyin mulkin Nijar.
Shugaban mulkin sojan Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya isa kasar Mali domin ganawa da takwaransa Kanar Assimi Goita, a ziyararsa ta farko da ya kai wata ƙasa tun bayan da ya ƙwace mulki a watan Yuli, kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rawaito a ranar Alhamis.
Ƙasashen Mali da Burkina Faso da ke maƙwabtaka da Nijar - wadanda su me sojojin da suka ƙwace mulki a shekarar 2020 da 2022 ke mulki a ƙasashen, sun yi alkawarin bayar da hadin kai ga jagororin juyin mulkin Nijar.
A cikin watan Satumba ne kasashen yankin Sahel guda uku suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar da ta ƙunshi tanadin kare juna a kan duk wani harin da za a kai kan ɗaya daga cikinsu.
Suna kuma shirin karfafa dangantakar tattalin arziki.
Haka kuma gwamnatocin sun haɗa kai wajen yaƙi da ta'addanci a ƙasashensu.