Shugaba Erdogan ya caccaki kungiyoyin watsa labaran duniya kan yadda suka yi watsi da kisan gillar da ake yi wa 'yan jarida a Zirin Gaza, ya bayyana Isra'ila a matsayin wadda ta yi rashin nasara a yaƙin da ake ci gaba da yi a yankin na Falasdinawa.
A taron TRT World Forum na shekara-shekara, shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya caccaki kafafen yada labarai na Yammacin Duniya da masu rajin kare hakkin 'yan jarida kan ƙin cewa komai a kisan 'yan jarida da ake yi a Gaza suna fakewa da kafa hujja da Hamas.
Shugaba Erdogan ya caccaki kungiyoyin watsa labaran duniya kan yadda suka yi watsi da kisan gillar da ake yi wa 'yan jarida a Zirin Gaza, inda ya bayyana Isra'ila a matsayin wadda ta yi rashin nasara a yaƙin da ake ci gaba da yi a yankin na Falasdinawa.
"Isra'ila tana kashe mata da yara ƙanana a Gaza har ma da 'yan jarida da ke kokarin gudanar da ayyuka a cikin mawuyacin hali," in ji Erdogan, a wajen ƙaddamar da babban taro karo na bakwai da aka gudanar a Istanbul a ranakun 8 da 9 ga watan Disamba.
"Sama da 'yan jarida 70 aka kashe a Gaza. Ina manyan kafafen watsa labaran duniya suke? Me ya sa ba sa ba da kanun labarai kan 'yan jaridun da aka kashe?" Shugaban na Turkiyya ya ce.
"Kowace rana ana kashe dan jarida, amma duk da haka ba mu ji wata magana daga cibiyoyin da suka shafe shekaru suna ɓaɓatun neman 'yancin 'yan jarida ba."
Taron yana gudana ne a Otel din Hilton Bomonti a birnin Istanbul, inda aka gudanar da jawabai masu sha'awa da fatan kawo sauyi.
Taken taron shi ne Haɓaka Tare: Nauyi da Ayyuka, da Matakai, ana shirya taron ne a matsayin wani wake na tattauna batutuwan da suka fi daukar hankali a duniya a yau.
Yawancin mahalarta taron a yau daliban jami'a ne. Hayat Bikana Beydi, mai shekaru 22, daga Habasha, tana karantar kimiyyar siyasa da huldar kasa da kasa a Jami'ar Istanbul.
"Maganar gaskiya ina farin cikin kasancewa a nan," Beydi ya fada kafin a fara taron da ƙarfe 1120 na safe agogon GMT. Wannan ita ce shekara ta hudu da ɗalibin Habashan ke halartar taron.
"Eh, saboda a nan mutane suna zuwa suna ba da labarin abubuwan da suka faru, muna son koyi da su saboda mutanen da suka zo nan sun fi mu ƙwarewa. Don haka mun koyi abubuwa da yawa a wurinsu."
"A cikin zuciyata ba ni da taƙamaiman wanda na fi so a cikin masu gabatar da jawabi, amma ina sa ran dukkansu za su kasance masu kyau," Beydi, wacce ta fara jin labarin taron daga shirin bayar da tallafin karatu a jami'a ta fada, ta ƙara da cewa taron ya kuma shafi karatunta.
Ta ƙara da cewa, "Saboda masana sun zo suna ba da labarin abubuwan da suka faru, kuma [a matsayinmu na dalibai], muna son a yi koyi da su saboda mutanen da suka zo nan suna da ƙwarewa sosai don raba."
Zahra Ismail Hussein, mai shekaru 23 daga Somaliya, tana da ra'ayi iri daya, inda ta ce jin yadda ƙawayenta ke magana kan abubuwan da suka faru a baya ya sa ta samu halartar wannan shekarar. "Ina ɗokin ganin na halarta na ga yadda abin yake, kuma ina fatan koyon ilimi daga masu jawabi," in ji Hussein.
TRT's Director-General Mehmet Zahid Sobaci kicks off the event with an opening speech, saying Palestine will be high on the agenda at the forum. He added that the world is witnessing a failure of humanity in Gaza.