Dollar

43,3792

0.03 %

Euro

51,4564

0.3 %

Gram Gold

7.099,7900

2.22 %

Quarter Gold

11.584,3300

0 %

Silver

152,7500

6.84 %

Da wahala a iya sanin adadin mutanen da aka kashe saboda fararen-hula da dama suna can sun ɓuya a cikin daji a yayin da ake ci gaba da rikici, a cewar wani shugaban ƙungiyar kare hakkin ɗan'adam ta cikin ƙasar.

Sabon rikici ya raba fiye da mutum 180,000 da muhallansu a Sudan ta Kudu

Sabon rikicin da ya ɓarke a Sudan ta Kudu ya raba mutum fiye da 180,000 da muhallansu, inda ganau suka ce ana harba bamabamai yayin da fararen-hula suke ci gaba da tserewa zuwa yankunan kurmi don kauce wa tashin hankali.

Ƙasar Sudan ta Kudu na fama da yaƙi da matsancin talauci da mummunan cin-hanci da rashawa tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 2011, amma yanzu rikici na neman yin ƙamari tsakanin ɓangarorin da ba-sa-ga-maciji da juna, inda suke fafatawa a jihar Jonglei da ke arewacin Juba, babban birnin ƙasar.

"Na rasa madafa kuma idan na rasa zaɓi, zan tsere zuwa yankin da ke da kurmi inda ya fi aminci," a cewar Daniel Deng, mai shekara 35, ɗaya daga cikin dubban mutanen da rikicin Jonglei ya shafa. Ya bayyana haka ne a tattaunawa ta wayar tarho da AFP.

Ya ƙara da cewa an tafka mummunan yaƙi a makon jiya a yankin Duk inda yake da zaman, bayan dakarun ‘yan adawa sun ƙwace iko da yankin ko da yake daga baya sojojin gwamnati sun kore su.

"An kashe mutane da dama," in ji Deng, wanda ya ƙiyasta cewa an kashe mayaƙa aƙalla 300, ko da yake AFP bai iya tabbatar da wannan iƙirari ba.

Yarjejeniyar raba madafun iko da aka ƙulla tsakanin ɓangarori biyu da ke yaƙi da juna ta fuskanci matsala bayan Shugaba Salva Kiir ya sa an kama daɗaɗɗen abokin hamayyarsa kuma mataimakin shugaban kasa, Riek Machar, a watan Maris inda yanzu yake fuskantar shari’a kan "laifukan take hakkin bil’adama".

Dakarunsu sun gwabza yaƙi sau da dama a cikin shekara ɗaya da ta wuce, amma a watan Disamba yaƙin ya tsananta a yankin Jonglei.

Hukumomi a Sudan ta Kudu sun ƙiyasta cewa mutanen da yaƙi ya raba da muhallansu sun zarta 180,000 a larduna huɗu na jihar Jonglei, a cewar hukumar OCHA da ke kula da bayar da agajin jinƙai ta MDD a wannan makon.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#