Dakarun Isra'ila sun ci gaba da luguden wuta a Gaza  ranar Juma'a jim kadan bayan wa'adin yarjejeniyar tsagaita wuta da suka kulla da Hamas ya kare.

Kasashen duniya za a dora wa alhakin laifukan yakin da Isra'ila take aikatawa a Gaza —  Gwamnatin Falasdinu

Gwamnatin Falasdinu da ke Gaza ta dora alhakin "laifukan yakin da Isra'ila take ci gaba da aikatawa" a kan kasashen duniya, a yayin da dakarun Isra'ila suka ci gaba da kaddamar da hare-hare a Gaza bayan karewar wa'adin yarjejeniyar tsagaita.

"Rundunar sojin Isra'ila da ke mamaya ta sake kaddamar da yaki mai muni a kan al'ummar Falasdinu da ke Zirin Gaza,” a cewar wata sanarwa da ofishin watsa labarai na gwamnati da ke Gaza ya fitar ranar Juma'a da safe.

Sojojin Isra'ila sun kai hare-hare a gidaje da dama da kuma kan fararen-hula a Gaza, in ji ofishin na watsa labarai, inda ya jaddada cewa: “Kasashen duniya ne za su dauki alhakin laifukan yakin da Isra'ila ke ci gaba da aikatawa a Zirin Gaza.”

Hukumomin lafiya a Gaza sun bayyana cewa luguden wutar da Isra'ila take ci daga da yi a yau ya kashe Falasdinawa 32.

Jiragen yakin Isra'ila sun kai hari kan fararen-hula da dama a Gaza da sayin safiyar Juma'a./Hoto:AA

“Kasashen duniya, musamman Amurka da shugabanta Joe Biden da Sakataren Harkokin Waje Antony Blinken, su ne da alhakin laifukan mamaya da na yakin da Isra'ila take aikawa a kan fararen-hula da kananan yara da mata a Gaza,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa: “An keta dokokin yaki da na kasashen duniya game da jinkai. Kasashen duniya sun bai wa Isra'ila damar ci gaba da kai hare-hare a Zirin Gaza.”

#