Wannan shafi yana kawo muku sabbin bayanai a ranar Talata, 14 ga watan Nuwamba, kan hare-haren da Isra'ila ke kai wa Gaza bayan Hamas ta kutsa kai Isra'ila inda ta kai mata hare-haren ba-zata a ranar 7 ga watan Oktoba.

KAI-TSAYE: Lauyoyin Falasdinawa sun shigar da Isra'ila kara a Kotun ICC

0750 GMT — Lauyoyin Falasdinawa sun shigar da Isra'ila kara a Kotun ICC

Lauyoyin wadanda hare-haren Isra'ila suka fadamawa a Gaza sun shigar da kara a Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya ICC da ke birnin Hague na Netherlands.

Wakilin jama'ar Gaza a kotun ICC wato Gilles Devers da wasu mutum hudu da suka masa rakiya domin kai korafin sun bayyana cewa Isra'ila ta aikata laifukan yaki a kan Gaza wadanda suka hada da kisan kare-dangi.

Isra'ila ta kashe sama da mutum 11,180 a Gaza wadanda akasarinsu yara ne tun daga 7 ga watan Oktoba.

#