Yaƙin da Tel Aviv ya kwashe shekara ɗaya yana yi a Gaza ya kashe Falasɗinawa aƙalla 42,065. A gefe guda, hare-haren da Isra'ila ta ke kai wa a Lebanon tun daga Oktoban 2023 sun kashe fiye da mutum 2,169 kana sun raba fiye da mutum 1.2 da muhallansu.

Kai-tsaye: Jiragen yaƙin Isra'ila sun kai munanan hare-hare a Yammacin Gaɓar Kogin Jordan da ta mamaye

Juma'a, 11 ga Oktoban 2024

0130 GMT — Jiragen yakin Isra'ila sun harba makamai masu linzami da suka kashe Falasdinawa biyu a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye.

Kamfanin dillancin labaran Falasdinu na WAFA ya rawaito cewa, an kashe 'yan kasar biyu a wani harin da jiragen yakin Isra'ila suka kai kan wata mota a yankin Jabal al Salihin da ke tsakanin yankin Dhannabah da kuma sansanin 'yan gudun hijira na Nur Shams da ke gabashin Tulkarem.

Majiyoyin sun kara da cewa nan take sojojin Isra'ila suka kai farmaki a yankin bayan sun kai farmakin, inda suka kwashe gawarwakin mutanen, sannan suka janye daga wurin.

Tun da fari da yammacin wannan rana ne sojojin Isra'ila suka kai farmaki kan sansanin 'yan gudun hijira na Nur Shams tare da ƙaƙaba wa sansanin ƙawanya kafin su kai hare-hare.

Karin bayani ????

0100 GMT — Manyan jami'an tsaron Isra'ila sun gana a cikin Lebanon

Rundunar sojin Isra'ila ta bayyana cewa, babban hafsan hafsoshin sojin kasar Herzi Halevi da daraktan Shin Bet Ronen Bar sun gudanar da wani bincike na hadin gwiwa a kudancin kasar Lebanon a karon farko.

Sanarwar da rundunar sojin ta fitar ta ce Halevi da Bar "sun gudanar da wani bincike na hadin gwiwa tare da dakarun da ke yaki a kudancin Lebanon, tare da kwamandan rundunar sojojin arewa da kuma kwamandan runduna ta 91."

A cewar jaridar Yedioth Ahronoth ta Isra'ila, wannan shi ne karo na farko da manyan jami'an tsaro ke gudanar da taro a cikin Lebanon.

#