A zantawa da TRT Afrika, ma’aikaciyar rigakafi, Dorothy Ezikiel, ta ce ‘’nakan tafi Mayo da Gombi, wadanda suke kimanin sa’a biyu daga wurin da nake zaune. Kafin na tafi, nakan yi addu’ar Allah Ya kare ni.’’

KAI-TSAYE: Isra'ila ta kashe manomi a sansanin 'yan gudun hijira

1100 GMT — Isra'ila ta kashe manomi a sansanin 'yan gudun hijira

Isra’ila ta kashe wani manomi da kuma ji wa wani rauni a wata gona da ke sansanin ‘yan gudun hijira ta Maghazi a Gaza.

Kungiyar bayar da agaji ta Red Crescent ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a yau Lahadi.

Wannan lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da aka shiga kwana na uku na yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma musayar fursunoni tsakanin Falasdinawa da kuma Isra’ila.

1045 GMT — Isra'ila ta kashe karin Falasdinawa biyu a Gabar Yamma da Kogin Jordan

Sojojin Isra'ila sun kara kashe Falasdinawa biyu a garuruwan Nablus da Jenin da ke Gabar Yamma da Kogin Jordan da Isra'ila ta mamaye, kamar yadda Ma'aikatar Lafiya ta tabbatar.

Isra'ila da Falasdinawa sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da musayar fursunoni ta kwanaki hudu. / Hoto: Reuters

Ma'aikatar Lafiyar ta ce a cikin sa'o'i 24, akalla Falasdinawa bakwai dakarun na Isra'ila suka kashe a cikin sa'o'i 24 a daidai lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Falasdinawa ta shiga kwana na uku.

A bangare guda kuma, gidan fursunan Isra'ila ya ce ya karbi jerin sunayen Falasdinawa 39 wadanda ake sa ran saki a ranar Lahadi, kamar yadda kafar watsa labarai ta Isra'ilar ta ruwaito.

#