Yaƙin Isra’ila a Zirin Gaza da aka mamaye ya shiga rana ta 250, ya kashe aƙalla Falasɗinawa 37,164 — kaso 71 mata da yara da jarirai — ya jikkata mutane 84,832, sannan an yi amanna fiye da mutum 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzan gidajen da aka ruguza.

Kai-tsaye: Amurka na 'nazartar' martanin Hamas kan sulhu yayin da Isra'ila ke ci gaba da yin luguden wuta a Gaza

2001 GMT — Amurka tana "nazari" kan martanin Hamas a hukumance ga shirin sulhu na baya-bayan nan a yankin Gaza da aka mamaye, a cewar Fadar White House.

Washington ta karɓi "martanin da Hamas ta miƙa wa Qatar da Masar kuma muna nazarinsa yanzu haka," kamar yadda Mai Magana da yawun Majalisar Tsaron Ƙasa John Kirby ya shaida wa 'yan jarida, yayin da ya ƙi ba da cikakken bayani kan abin da martanin ya ƙunsa.

Mai magana da yawun Hamas Jihad Taha ya ce martanin ya ƙunshi "yin kwaskwarima da za ta tabbatar da tsagaita wuta da janyewar Isra'ila da sake gina Gaza da kuma musayar fursunoni." Shi ma Taha bai yi ƙarin bayani ba.

Sai dai yayin da suke goyon bayan yarjejeniyar, jami'an Hamas sun bayyana damuwa kan ko Isra'ila za ta yi aiki da sharuɗan, musammanma tanadin kawo ƙarshen yaƙi na dindindin, da ficewar Isra'ila daga Gaza baki ɗaya inda za a sako gaba ɗaya mutanen da ƙungiyar ta fafutuka take garkuwa da su.

Duk da cewa Amurka ta ce Isra'ila ta karɓi tayin, Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya nuna alamun baki-biyu, yana cewa Isra'ila ba za ta tsaya ba har sai ruguza Hamas.

2239 GMT — Hamas ta ambaci martaninta kan sulhu a matsayin na 'gaske ma cike fata'

Martanin Hamas ga ƙudurin yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza "ya buɗe wata babbar hanya" ta cim ma yarjejeniya, a cewar wata mamba a ɓangaren Hamas na siyasa Izzat al-Risha.

Martanin ƙungiyar "na sanin ya kamata ne, na gaske sannan mai cike da fata," a cewar al-Rishaq a cikin wata sanarwa.

#