Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce, wannan rana ta hadin kai ta kasa da kasa ta zo ne a wani babi mafi duhu a tarihin al'ummar Falasdinu.

Hotuna: Dubban mutane sun yi zanga-zangar don bikin Ranar Nuna Goyon Bayan Falasdinu ta Duniya

Dubban mutane ne a fadin duniya suka gudanar da bikin ranar nuna goyon baya ga al'ummar Falasdinu a ranar Laraba, inda suka buƙaci a kawo karshen cin zarafin da Isra'ila ke yi kan al'ummar Falasdinawa, tare da yin kira da a samar da 'yantacciyar kasar Falasdinu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres a cikin wani sako ya ce "Wannan ranar hadin kai ta kasa da kasa ta zo ne a wani babi mafi duhu a tarihin al'ummar Falasdinu."

Guterres ya kuma yi nuni da wani muhimmin aiki na hukumar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da 'yan gudun hijirar Falasdinu, UNRWA, yana mai cewa a halin yanzu ya fi "muhimmanci fiye da kowane lokaci" cewa kasashen duniya su tsaya tare da hukumar a matsayin tushen tallafi ga al'ummar Falasdinu.

Masu fafutuka masu goyon bayan Falasdinu sun dinga ɗaga tutoci suna kira ga gwamnatin Burtaniya da ta bukaci a tsagaita wuta a Gaza da kuma dakatar da sayar da makamai ga Isra'ila, a gaban majalisar dokokin da ke gadar Westminster a London ranar 29 ga Nuwamba, 2023.  (Palestine Action/Reel News/via Reuters)
Masu fafutuka na Philippines sun gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasdinawa a birnin Quezon, Metro Manila, Philippines.
Wata yarinya tana rike da tutar Falasdinu don bikin ranar goyon bayan al'ummar Falasdinu, kusa da ginin ESCWA, a Beirut, Lebanon, a ranar 29 ga Nuwamba.
Mutane sun gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga al'ummar Falasdinu a Karachi, Pakistan a ranar 29 ga Nuwamba, 2023. / Hoto: Faizan Lakhani
Wani mai fafutuka mai goyon bayan Falasdinu ya rike wata alama da ke nuna hadin kai tare da mutane daga kabilu daban-daban na duniya, yayin da yake sanye da wata sutura ta asalin Amurka, a lokacin wata zanga-zangar nuna goyon bayan Falasdinu da jam'iyyun siyasa daban-daban da kungiyoyin kwadago suka yi a Johannesburg a ranar 29 ga Nuwamba, 2023.
#