Sport
Dollar
0,0000
%Euro
0,0000
%Gram Gold
0,0000
%Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Kamfanin dillancin labaran AFP ya ambato shugaban yana cewa ana tunanin cewa 86 daga cikinsu suna hannun masu garkuwa da mutane kawo yanzu.
Masu ibada Kiristoci 166 da ake fargabar ‘yanbindiga sun yi garkuwa da su a ƙauyen Kurmin Wali na Jihar Kaduna da ke arewacin Nijeriya a watan da ya gabata sun koma gida, bayan sun tsere a lokacin harin domin fakewa a wasu ƙauyuka, kamar yadda wani shugaban al’umma ya bayyana ranar Lahadi.
Kamfanin dillancin labaran AFP ya ambato shugaban yana cewa ana tunanin cewa mutum 86 daga cikinsu suna hannun masu garkuwa da mutane kawo yanzu.
Garkuwa da mutane da aka yi ranar 18 ga watan Janairu a lokacin ibadan ranar Lahadi a coci-coci guda uku ita ce ta baya bayan nan a cikin jerin satar mutane da ake yi wa Musulmai da Kiristoci a Nijeriya.
Hare-haren sun ƙara matsin lamba na ƙasashen duniya kan gwamnatin Nijeriya.
Ishaku Dan'azumi, wani shugaba a ƙauyen Kurmin Wali kuma babban limamin addini, ya ce an yi garkuwa da mutane 177 a harin da ‘yanbindiga suka kai, inda mutum 11 kawai suka tsere.
Ranar Lahadi ya bayyana wa AFP cewa daga cikin mutane 166 da ba a san inda suke ba, 80 sun riga sun koma gida.
"Mun ɗauka dukkan mutum 166 da suka ɓata ne aka yi garkuwa da su," kamar yadda ya shaida wa AFP ta waya daga ƙauyensa.
"Amma sai ya zamana wasu sun tsere kuma sun nemi mafaka a wasu ƙauyuka," in ji shi. "Ta bayyana cewa mutum 86 ne ke hannun masu garkuwa da mutane."
'Tserewa cikin daji'
Godiya Ayuba, mai shekara 34 uwa ga ‘ya’ya shida, wadda ta koma Kurmin Wali ranar Lahadi, ta ce ta tsere, inda ta shafe awannin tana tafiya a cikin daji da gonaki kafin ta kai wani ƙauyen na daban.
"Mun ga ‘yanbindigar sun nufi cocin kuma wasu daga cikinmu sun samu sun tsere cikin daji," kamar yadda ta shaida wa AFP. "Na ci gaba da gudu kuma na rage gudu da na yi nesa daga ƙauyen," kamar yadda ta shaida wa AFP. Bayan wayarta ta faɗi a kan hanya, ta rasa yada za ta tuntuɓi iyalinta. ‘Yan ƙauyen da suka karɓe ta sun taimaka mata wajen komawa gida.
"Na isa gida yau. Na yi murna kuma na yi baƙin ciki saboda na gano cewa biyu daga cikin ‘ya’yana suna cikin waɗanda aka yi garkuwa da su...Ina addu’ar dawowarsu cikin aminci da sauran mutanen da ‘yanbindiga suka yi garkuwa da su."
Ana tunanin cewa ‘yandaban da ake ce wa ‘ɓarayin daji’ ne suka yi garkuwa da mutanen.
Bayan suka ta diflomasiyya game da abin da shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa kisan kiyashi ne musamman kan Kiristoci, Amurka ta ƙaddamar da hare-hare a Nijeriya kan ‘yanbindiga da hukumomi suka ce ke da alaƙa da ƙungiyar IS.
Amma harin da aka kai sau ɗaya bai hana hare-hare ba a ƙasar ta yammacin Afirka.
A arewacin ƙasar, tana fama da masu iƙirarin jahadi da ɓarayin daji da kuma rikicin manoma da makiyaya kan fili da albarkatu.
Garkuwa da mutane da yawa da aka yi a Kaduna ta biyo bayan wata garkuwa da aka yi da kuma sake ‘yan makarantar ɗarkiar katolika a jihar Neja mai maƙwabtaka a ƙarshen shekarar da ta gabata.
Comments
No comments Yet
Comment