Osimhen, wanda yanzu shi ne zakaran kwallon kafar Italiya, ya doke dan wasan Liverpool da Masar Mohamed Salah da dan wasan Paris Saint-Germain da Maroko Achraf Hakimi inda ya lashe kyautar.
'Yan Nijeriya Victor Osimhen da Asisat Oshoala sun lashe kyautar gwarazan 'yan kwallon Afirka na CAF 2023 a rukunin maza da mata a bikin da aka gudanar a Marrakech, babban birnin Maroko ranar Litinin da maraice.
Osimhen, wanda yanzu shi ne zakaran kwallon kafar Italiya, ya doke dan wasan Liverpool da Masar Mohamed Salah da dan wasan Paris Saint-Germain da Maroko Achraf Hakimi inda ya lashe kyautar.
Oshoala, mai shekara 29, tana cikn 'yan wasan Nijeriya mata da suka kai zagayen 'yan-goma-sha-shida a Gasar Kwallon Kafa ta FIFA da aka gudanar a bazara a kasashen Australia da New Zealand ko da yake Ingila ta fitar da su daga gasar.