Wata majiyar tsaro ta ce wasu mutane ɗauke da makamai sun kai hari a cikin harabar fadar shugaban kasar, sai dai mai magana da yawun fadar shugaban ƙasar Abderaman Koulamallah ya ce komai ya lafa.
An ji ƙarar harbe-harben bindiga da yammacin Laraba a kusa da fadar shugaban kasa a N'Djamena babban birnin kasar Chadi. Rahotanni sun ce an jibge tankokin yaki da jami'an tsaro a kan tituna.
Wata majiyar tsaro ta ce wasu mutane ɗauke da makamai sun kai hari a cikin harabar fadar shugaban kasar, sai dai mai magana da yawun fadar shugaban ƙasar Abderaman Koulamallah ya ce komai ya lafa.
An toshe dukkan hanyoyin da ke zuwa fadar shugaban kasa, ana kuma iya ganin tankokin yaki a kan titunan babban birnin kasar, kamar kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito.
Wannan lamarin na zuwa ne ƙasa da makonni biyu bayan gudanar da zaɓen ‘yan majalisa a ƙasar.