Dollar

41,0307

-0.03 %

Euro

48,1154

0.6 %

Gram Gold

4.510,7100

0.62 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Ɗaruruwan mutane sun rasa muhallansu a Jihar River Nile sannan gomman gine-gine sun rushe sakamakon ruwan sama mai ƙarfi.

Ambaliyar ruwa ta rusa gidaje a ƙauyuka da dama na Sudan

Akalla mutane 14 sun rasa rayukansu sakamakon ruwan sama mai karfi da ambaliyar ruwa a arewaci da kudu maso gabashin Sudan, kamar yadda kafafen yada labarai na cikin gida suka bayyana a ranar Laraba.

Shaidu sun ce ruwan sama mai ƙarfi da ambaliyar ruwa sun lalata garuruwa da ƙauyuka da dama a Jihar River Nile, wanda ya haifar da katsewar wutar lantarki da kuma rushewar gine-gine da dama, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na jihar, SUNA, ya ruwaito.

Mutane shida sun rasu lokacin da gidaje suka rushe sakamakon ruwan sama mai ƙarfi a arewacin Jihar River Nile.

Wata uwa da 'ya'yanta uku sun mutu a Jihar Sennar da ke kudancin Sudan bayan ɗakin gidansu ya rushe sakamakon ruwan sama mai karfi.

Mutane sun rasa matsuguni

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#