Sport
Dollar
43,4990
0.19 %Euro
51,6240
-0.9 %Gram Gold
6.788,9600
-9.85 %Quarter Gold
12.225,8700
-6.97 %Silver
116,5000
-28.39 %Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya sake tabbatar da matsayar Iran ta rashin sha'awar ƙera makamin nukiliya da kuma buɗe ƙofofinta domin tattaunawar diflomasiyya, a wata ziyara da ya kai Turkiyya.
A “shirye” Tehran take don "yarjejeniya ta nukiliya mai adalci da daidaito," kuma "ba ta taɓa" neman ƙera makamin nukiliya ba, in ji Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi yayin ganawarsa da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da Ministan Harkokin Waje Hakan Fidan.
“A cikin tattaunawar mu (a ranar Juma'a), na sake jaddada cewa Iran ba ta taɓa neman ƙera makamin nukiliya ba kuma tana a shirye ta rungumi yarjejeniya ta nukiliya wadda ke cike da adalci kuma ta dace da muradun al'ummarmu; wannan ya haɗa da tabbatar da 'Babu Makaman Nukiliya' da kuma tabbatar da ɗage takunkumi,” in ji Araghchi a shafin X a ranar Asabar.
A yayin da yake bayyana gamsuwarsa da tattaunawar kan dangantakar Turkiyya da Iran da batutuwan yankin da suka shafe su duka, ya lura cewa, tare da wasu ƙasashe 'yan uwa, Ankara ta ba da taimako domin inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
“Tehran na godiya ga irin wannan ƙoƙari kuma tana maraba da su,” in ji Araghchi, yana bayyana shirin Tehran na aiki tare da ƙasashen yankin don kawo kwanciyar hankali da zaman lafiya a yankin da kuma "kare shi daga haramtaccen farmaki."
Tattaunawar tsakanin Araghchi da jami'an Turkiyya na zuwa ne yayin da ministan harkokin wajen Iran ya ziyarci Turkiyya a ranar Juma'a.
A halin da ake ciki, Shugaban Iran Masoud Pezeshkian a ranar Asabar ya ce Shugaban Amurka Donald Trump da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da Turai sun rura wutar tashin hankali a zanga-zangar da kwanan nan ta mamaye ƙasar wadda kuma ta “fusata” jama’a.
Comments
No comments Yet
Comment