Jihar Benue na fama da ƙarin hare-haren 'yan bindiga a baya bayan nan, waɗanda ake alaƙantawa da makiyaya.
Gwamnatin Benue da ke tsakiyar Nijeriya ta ce mutum aƙalla 30 ne suka mutu sakamakon harin da wasu 'yan bindiga suka kai ranar Juma'a da daddare a wani ƙauyen na jihar.
Kwamishinan Watsa Labarai na jihar Matthew Aboh ne ya tabbatar da mutuwar mutum 30 a harin da 'yan bindiga suka kai a ƙauyen Ayati.
Sai dai wasu rahotanni sun ce waɗanda aka kashe za su kai 50.
Jihar Benue na fama da ƙarin hare-haren 'yan bindiga a baya bayan nan, waɗanda ake alaƙantawa da makiyaya.
A watan jiya, wani hari da 'yan bindiga suka kai a jihar ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 25.
Nijeriya ta daɗe tana fama da hare-haren 'yan bindiga da na ƙungiyoyin 'yan ta'adda irin su Boko Haram da ISWAP.