Amurka za ta ci gaba da tattaunawa da Iran kan shirin nukiliya

Trump: Babu yarjejeniya da aka cim ma bayan ganawa da Netanyahu

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba a cim ma wani takamaiman abu ba yayin ganawarsa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, sai dai ya nanata cewa za a ci gaba da tattaunawa da Iran domin duba yiwuwar ƙulla wata yarjejeniya. TRT Hausa

Trump ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social bayan ganawar da suka yi a Fadar White House, inda ya ce abin da ya fi so shi ne a samu yarjejeniya ta diflomasiyya da Iran, amma idan hakan bai yiwu ba, dole a fuskanci sakamakon. TRT Hausa

Ya ce sun kuma tattauna kan ci-gaban da ake samu a Gaza da kuma halin da yankin Gabas ta Tsakiya ke ciki baki ɗaya. TRT Hausa

A nasa ɓangaren, ofishin Netanyahu ya ce Firaministan Isra’ila ya jaddada batun tsaron Isra’ila yayin tattaunawar da Trump kan shirin nukiliyar Iran. TRT Hausa

Ganawar, wacce ita ce ta bakwai tsakanin shugabannin biyu tun bayan Trump ya koma mulki, an yi ta ne a ɓoye, inda aka hana manema labarai shiga, kuma Netanyahu ya bar fadar ba tare da faretin ban-girman da aka saba yi wa baƙi ba. TRT Hausa

Washington da Tehran sun sake soma tattaunawar nukiliya a makon jiya a Oman, bayan da aka dakatar da su sakamakon hare-haren sama da Amurka ta kai kan wasu wuraren nukiliyar Iran a lokacin rikicin kwanaki 12 da ya auku a bara. TRT Hausa

 
 
 
 
 
#