Sport
Dollar
40,4343
0.24 %Euro
47,1614
0.49 %Gram Gold
4.349,9900
0.54 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%An cim ma yarjejeniyar ne bayan ɓangarorin biyu sun shafe watanni uku suna tattaunawa a Doha babban birnin Qatar.
Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da ƙungiyar 'yan tawayen M23 da ake zargin tana samun goyon bayan Rwanda, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta a ranar Asabar, domin kawo ƙarshen rikicin da ya addabi gabashin ƙasar mai arzikin ma’adanai amma cike da rikice-rikice.
An cim ma yarjejeniyar ne bayan ɓangarorin biyu sun shafe watanni uku suna tattaunawa a Doha babban birnin Qatar. Wannan na zuwa ne bayan wata yarjejeniya ta daban da aka cim ma tsakanin Congo da Rwanda a birnin Washington a watan da ya gabata.
Kungiyar M23, wadda ta mamaye manyan yankuna a gabashin DRC cikin wata guda a watan Janairu da Fabrairu, inda ta dage kan cewa tana son ƙulla yarjejeniya ta musamman da gwamnatin Kinshasa, saboda yarjejeniyar Washington ta bar wasu "muhimman matsaloli" a gefe.
Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yaba da wannan ci gaba, tana mai cewa:
"Wannan muhimmin ci gaba ne da ke nuna sahihancin ƙoƙarin kawo zaman lafiya da dawwamammen tsaro a gabashin DRC da kuma yankin Great Lakes
A cewar yarjejeniyar, bangarorin sun kuma amince da fara tattaunawa don ƙulla cikakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya, tare da samar da taswirar dawo da ikon gwamnati a yankunan gabashin DRC da ke ƙarƙashin ikon ‘yan tawaye.
Comments
No comments Yet
Comment