Dollar

40,4343

0.24 %

Euro

47,1614

0.49 %

Gram Gold

4.349,9900

0.54 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

An cim ma yarjejeniyar ne bayan ɓangarorin biyu sun shafe watanni uku suna tattaunawa a Doha babban birnin Qatar.

Jamhuriyyar Kongo da 'yan tawayen M23 sun cim ma yarjejeniya domin dakatar da rikici a gabashin DRC

Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da ƙungiyar 'yan tawayen M23 da ake zargin tana samun goyon bayan Rwanda, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta a ranar Asabar, domin kawo ƙarshen rikicin da ya addabi gabashin ƙasar mai arzikin ma’adanai amma cike da rikice-rikice.

An cim ma yarjejeniyar ne bayan ɓangarorin biyu sun shafe watanni uku suna tattaunawa a Doha babban birnin Qatar. Wannan na zuwa ne bayan wata yarjejeniya ta daban da aka cim ma tsakanin Congo da Rwanda a birnin Washington a watan da ya gabata.

Kungiyar M23, wadda ta mamaye manyan yankuna a gabashin DRC cikin wata guda a watan Janairu da Fabrairu, inda ta dage kan cewa tana son ƙulla yarjejeniya ta musamman da gwamnatin Kinshasa, saboda yarjejeniyar Washington ta bar wasu "muhimman matsaloli" a gefe.

Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yaba da wannan ci gaba, tana mai cewa:

"Wannan muhimmin ci gaba ne da ke nuna sahihancin ƙoƙarin kawo zaman lafiya da dawwamammen tsaro a gabashin DRC da kuma yankin Great Lakes

A cewar yarjejeniyar, bangarorin sun kuma amince da fara tattaunawa don ƙulla cikakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya, tare da samar da taswirar dawo da ikon gwamnati a yankunan gabashin DRC da ke ƙarƙashin ikon ‘yan tawaye.

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#