Publication : 26 January 2026
Update : 26 January 2026
Tehran ta ce sojojinta suna cikin shirin ko-ta-kwana yayin da sojojin Amurka ke tunkaro Gabas ta Tsakiya
Iran ta yi gargaɗin cewa za ta ɗauki duk wani hari a kanta a matsayin “cikakken yaƙi,” yayin da ake sa ran isowar kayan aikin soji na Amurka zuwa Gabas ta Tsakiya cikin ‘yan kwanaki masu zuwa. Wani jami’in Iran mai mukami ya ce an sanya sojojin ƙasar cikin shirin ko-ta-kwana saboda yiwuwar barazana. (TRT Hausa)
Jami’in, wanda ya buƙaci a ɓoye sunansa, ya ce isowar jiragen ruwan yaƙi na Amurka ciki har da na ɗaukar jiragen saman yaƙi na iya zama barazana, duk da cewa Iran na fatan hakan ba zai kai ga fito-na-fito ba. Ya jaddada cewa sojojin Iran sun shirya fuskantar duk wani abu mafi muni. (TRT Hausa)
Ya ƙara da cewa Tehran ba za ta bambance girma ko ƙanƙantar hari ba, yana mai cewa duk wani farmaki za a mayar masa da martani cikin ƙarfi. (TRT Hausa)
A wani ɓangare, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka na da jirgin ruwan dakon jiragen sama da ke kan hanyarsa zuwa yankin, amma ya bayyana fatan cewa ba za a yi amfani da shi ba. A halin yanzu, jiragen ruwan yaƙin Amurka da jiragen saman yaƙi sun fara motsi a tekun Asia-Pacific. (TRT Hausa)
Jami’in Iran ya jaddada cewa idan Amurka ta keta ‘yancin kai da ikon yankin Iran, to Tehran za ta yi amfani da dukkan hanyoyin da take da su wajen mayar da martani domin kare kanta da dawo da daidaito. (TRT Hausa)
Migration: South Africa to relocate refugee centres to border entry points
President Cyril Ramaphosa says South Africa cannot tackle migration challenges alone, and has called for greater cooperation across the continent.
Davido, Burna Boy, Rema and Tyla set for 2026 World Cup
Davido has been selected to headline the official FIFA World Cup Countdown Concert on 10 June, 2026 in Los Angeles, United States.
Mauritius rejects reported US proposal to purchase Chagos Islands
Mauritius maintains its its sovereignty over the Chagos Islands is non-negotiable.
Most Read
All rights reserved. Newstimetr © 2023