Publication : 10 March 2026
Update : 10 March 2026
Dauda Lawal ya fice daga PDP sakamakon rikicin cikin gida
Gwamnan Jihar Zamfara a Nijeriya, Dauda Lawal, ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki a ƙasar, sakamakon rikicin cikin gida da ke addabar jam’iyyar.
An bayyana matakin ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau, inda mataimakin gwamnan jihar, Mani Mummuni, ya wakilci gwamnan wajen sanar da shawarar.
Mataimakin gwamnan ya ce an dauki matakin ne bayan shawarwari masu zurfi da kuma nazari kan halin da jam’iyyar PDP ke ciki, musamman dangane da bukatar hadin kai domin magance matsalolin tsaro a jihar.
Ya kuma umarci dukkan masu rike da mukaman siyasa da ke goyon bayan gwamnan da su ajiye mukamansu na PDP, sannan su shirya yin rajista da APC da zarar an bude rajistar sabbin mambobi.
Shugabannin siyasar jihar sun kuma bayyana burin kara rajistar sabbin mambobin APC har 400,000 a cikin kwanaki 17 masu zuwa a Zamfara.
Matakin ya biyo bayan tuntuba da shawarwari da gwamnan ya fara tun watan Janairu domin duba makomar siyasar jihar yayin da ake shirin babban zaben 2027.
Gwamna Lawal ya gode wa jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi na tsayawa takarar gwamna a zaben 2023, tare da cewa duk da sauyin jam’iyya, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da manufofin “Rescue Agenda” kamar yadda aka tsara.
Tushen labari: Newstimehub
Migration: South Africa to relocate refugee centres to border entry points
President Cyril Ramaphosa says South Africa cannot tackle migration challenges alone, and has called for greater cooperation across the continent.
Davido, Burna Boy, Rema and Tyla set for 2026 World Cup
Davido has been selected to headline the official FIFA World Cup Countdown Concert on 10 June, 2026 in Los Angeles, United States.
Mauritius rejects reported US proposal to purchase Chagos Islands
Mauritius maintains its its sovereignty over the Chagos Islands is non-negotiable.
Most Read
All rights reserved. Newstimetr © 2023